Jarumin Ali Nuhu yace Riga-kafin yara da kula da mata masu juna-biyu hakki ne a kan kowa.
Shugaban hukumar kula da harkokin fina finai ta Nijeriya kuma fitacce jarumi a masana’antar shirya fina finai ta KANNYWOOD, Ali Nuhu Muhammad ya ce iyaye da al’umma nada rawar da zasu taka wajen magance yawan mace macen mata a yayin haihuwa da mutuwar kananan yara.
Ali Nuhu ya kuma kara yin kira ga iyaye wajen kula da rigakafin ‘ya’yansu inda ya bayyana cewa rigakafi yafi magani.
” Abu ne da ya dace ga mutum ya dinga kai ‘ya’yansa rigakafi kafin komai. Wasu yaran suna ganin baiken iyayensu idan suka girma saboda sun gaza wajen kula dasu suna kanana.
“Kasancewa ta jakadan UNICEF na duniya, ina abubuwa da dama tare dasu. Kuma zan ci gaba da taka rawa. Ina fadakarwa a shafukan sada zumunta, dukkan bayanan da suke wajena ina kokarin isar da su.
Sannan yayi kira ga gwamnatoci da su mayar da hankali wajen inganta cibiyoyin lafiya a matakin farko don kula da mata da kananan yara.
Daily Nigerian Hausa



